Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    1,357 Pakistani Pilgrims Arrive in Madinah as Hajj 2026 Airlift Commences

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Saudi Arabia Plans Massive Airlift with 12,000+ Flights for Pilgrims

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Health Workers Invited to Join Volunteer Programme

    April 17, 2026

    Saudi Arabia Unveils Major Mina Expansion to Boost Pilgrim Capacity

    April 15, 2026

    Hajj Without Permit Violates Shariah Principles – Sheikh Sudais

    April 15, 2026
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Commences Vaccination of 965 Pilgrims Ahead of 2026 Hajj- By Abdulkadir Aliyu

    April 25, 2026

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024
  • Nahcon

    FG Weighs Policy Options to Cushion Aviation Fuel Costs, Assures Seamless 2026 Hajj Airlift

    April 30, 2026

    Hajj 2026: Inaugural Flight to Takeoff 3rd May – NAHCON

    April 28, 2026

    Kogi Clerics Hail NAHCON Chairman, Seek Sectoral Reforms

    April 26, 2026

    NAHCON Inaugurates Media Team for Hajj 2026, Urges Professionalism and Collaboration

    April 21, 2026

    NAHCON Warns Public Against Fake Hajj Visa Claims, Announces Closure of 2026 Visa Issuance

    April 15, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Gov Ahmad Aliyu and His Transformational Contributions to Hajj Administration in Sokoto

    March 23, 2026

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Shugaban Hukumar NAHCON Ya Bayyana Cigaban Da Ya Samar Cikin Kwanaki 100, Ya Bukaci Maniyyata Su Ba Da Hadin Kai – Daga Nura Ahmad Dakata
Hausa

Shugaban Hukumar NAHCON Ya Bayyana Cigaban Da Ya Samar Cikin Kwanaki 100, Ya Bukaci Maniyyata Su Ba Da Hadin Kai – Daga Nura Ahmad Dakata

adminBy adminJanuary 4, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
Professor Abdallahi Sale
Professor Abdallahi Sale

Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Farfesa Abdullahi Sale Usman, ya bayyana muhimman nasarorin da hukumar ta samu a karkashin jagorancinsa a cikin kwanaki 100 na farkon jagorancinsa

 

A wata tattaunawa ta musamman da wakilinmu, Kano Farfesa Sale Usman, ya jaddada muhimmancin koyi da shugabancin da ya gabata, inda ya ce, “A rayuwa duk wanda ya riga ka mulki, ko ya yi kura-kurai, ko ya yi nasara, sai ka yi addu’a Allah ya karba nasa ayyukan alheri kuma ya gafarta masa kurakuransa. Muna yin iya kokarinmu a yanzu kuma muna addu’ar Allah Ya taimakemu mu ci gaba da tafiya kan hanya madaidaiciya”.

 

Ya kuma bayyana cewa shugabancinsa yana daukar darasi daga ayyukan magabata, da amfani da nasarorin da suka samu da kuma gujewa kura-kuransu.

 

Da yake yin tsokaci kan hakan, ya ce, “A cikin kwanaki 100 da muka yi muna shugabanci, mun cimma yarjejeniya da kamfanonin jiragen sama na rage farashin tikitin jirgin sama idan aka kwatanta da wanda aka biya a bara. Mun kuma amince da yadda za a rika biyan kudin a Naira maimakon Dalar Amurka, wanda hakan wani gagarumin ci gaba ne.”

 

Farfesa Sale Usman ya bayyana wata babbar nasara: karbo sama da naira biliyan biyar na ayyukan da ba a yi wa maniyyata aikin hajjin 2023 ba daga hukumomin Saudia. Ya bayyana hakan ne a matsayin wani bangare na kokarin hukumar na tabbatar da bin doka da kuma kare muradun alhazan Najeriya.

 

Dangane da batun Fasfo da biza kuwa, shugaban hukumar ta NAHCON ya bayyana cewa hukumar na aiki kafada da kafada da hukumar kula da shige da fice ta kasa domin tabbatar da bayar da Fasfo na maniyyata a kan lokaci. Ya ce, “Suna ba mu haɗin kai, kuma muna samun ci gaba sosai a wannan batun.”

 

Day a juya kan batun tsarin biza, Farfesa Sale Usman ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa hukumomin Saudiyya sun shirya tsaf don magance matsalolin NAHCON. Ya yi nuni da cewa a yanzu babban abin da hukumar ta fi mayar da hankali a kai shi ne warware matsalolin da suka shafi takardar izinin Umrah. “Ta hanyar ofishin Ministan Harkokin Waje, mun gayyaci Ministan Hajji na Saudiyya zuwa Najeriya don magance duk wasu batutuwan da suka shafi Umrah,” inji shi.

 

Shugaban ya kuma yi kira ga masu niyyar zuwa aikin Hajji da su tabbatar da biyan kudin aikin Hajji a kan lokaci, yana mai jaddada cewa yin jirkirin biya yana kawo cikas ga tsare-tsare da manufofi. Ya yi kira ga masu irin wannan halayya da su daina domin a samu aiki mai inganci.

 

Da wannan kokari, Farfesa Abdullahi Sale Usman ya tabbatar da aniyar NAHCON na inganta aikin Hajji ga daukacin alhazan Najeriya, yayin da ya bukaci masu ruwa da tsaki da su goyi bayan ayyukan hukumar.

100 Days NAHCON Professor Abdullahi Saleh Usman
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Hajjin 2026: Sama da Ma’aikatan Lafiya 700 da Motocin Asibiti 90 Sun Shirya a Madinah

May 2, 2026

Hajjin 2026: Saudiyya Ta Kaddamar da Horaswa Ga Malamai da Jagororin Maniyyata a Madina

May 2, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Hausa

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

By adminMay 4, 20260

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa za ta fara jigilar…

Hajj 2026: Sokoto Hajj Delegation Inspects Hajj Terminal

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Hajj 2026: Sokoto Hajj Delegation Inspects Hajj Terminal

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.