Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    1,357 Pakistani Pilgrims Arrive in Madinah as Hajj 2026 Airlift Commences

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Saudi Arabia Plans Massive Airlift with 12,000+ Flights for Pilgrims

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Health Workers Invited to Join Volunteer Programme

    April 17, 2026

    Saudi Arabia Unveils Major Mina Expansion to Boost Pilgrim Capacity

    April 15, 2026

    Hajj Without Permit Violates Shariah Principles – Sheikh Sudais

    April 15, 2026
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Commences Vaccination of 965 Pilgrims Ahead of 2026 Hajj- By Abdulkadir Aliyu

    April 25, 2026

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024
  • Nahcon

    FG Weighs Policy Options to Cushion Aviation Fuel Costs, Assures Seamless 2026 Hajj Airlift

    April 30, 2026

    Hajj 2026: Inaugural Flight to Takeoff 3rd May – NAHCON

    April 28, 2026

    Kogi Clerics Hail NAHCON Chairman, Seek Sectoral Reforms

    April 26, 2026

    NAHCON Inaugurates Media Team for Hajj 2026, Urges Professionalism and Collaboration

    April 21, 2026

    NAHCON Warns Public Against Fake Hajj Visa Claims, Announces Closure of 2026 Visa Issuance

    April 15, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Gov Ahmad Aliyu and His Transformational Contributions to Hajj Administration in Sokoto

    March 23, 2026

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Tinubu, Shettima Sun Sake Jaddada Goyon Bayan NAHCON Kan Saukaka Hajjin 2026
Hausa

Tinubu, Shettima Sun Sake Jaddada Goyon Bayan NAHCON Kan Saukaka Hajjin 2026

adminBy adminNovember 11, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
IMG 20251017 210154

Daga Shafi’i Sani Mohammed Hukumar Kula da Ayyukan Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta ƙara ɗaukar matakai na musamman domin shirya Hajjin 2026 tare da cikakken goyon bayan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima, domin samar da farashi mai rahusa, sauƙin tafiya, da kuma ibada mai armashi ga alhazai ‘yan Najeriya.

A karkashin jagorancin Shugaban Hukumar kuma Babban Jami’in Gudanarwarta,  Farfesa Abdullahi Saleh Usman, Hukumar ta fara aiwatar da tsare-tsaren inganta ayyuka, haɓaka hidima, da rage kuɗaɗen da alhazai ke biya.

Dangane da umarnin Shugaba Tinubu na sauƙaƙa kudin aikin Hajji, NAHCON ta sanar da muhimmiyar ragi a farashin Hajj na shekarar 2026.

Sabbin farashin sune:
• ₦7,579,020.96 – Shiyyar Borno/Adamawa
• ₦7,696,769.76 – Shiyyar Arewa
• ₦7,991,141.76 – Shiyyar Kudu

Wannan raguwar tana tsakanin ₦748,000 zuwa ₦793,000 idan aka kwatanta da farashin bara kuma Farfesa Usman ya bayyana hakan a matsayin “shaida ta nuna damuwar gwamnati ga alhazai na Najeriya.”

Ya yabawa Shugaba Tinubu bisa wannan umarni na tausayi da kuma Mataimakinsa Shettima bisa kulawa ta kusa da yake yi wa ayyukan Hukumar, yana mai cewa goyon bayansu ya ƙara kwarin gwiwa wajen ci gaba da sauye-sauyen da ake aiwatarwa.

Domin bai wa mutane damar shiri da wuri, Hukumar ta sanya 5 ga Disamba, 2025 a matsayin ranar ƙarshe da za a karɓi kuɗin alhazai, tare da kira ga masu niyyar tafiya su biya da wuri domin samun sauƙin aiwatar da biza da sauran shirye-shirye.

A wani bangare na shirye-shiryen farkon shekara, tawagar Najeriya ƙarƙashin jagorancin Farfesa Usman ta halarci Hajj and Umrah Expo da aka gudanar a ranar 9 ga Nuwamba 2025 a Jeddah, Saudiyya.

Taron ya tara manyan masu ruwa da tsaki na Duniya kan harkokin Hajj da Umrah, inda ya kasance dama ga NAHCON wajen ƙarfafa alaƙa da gano sababbin hanyoyin gudanar da ibada.

Tun da farko, Najeriya ta rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) ta Hajj da Umrah ta shekara ta 2026 tare da Ma’aikatar Hajj da Umrah ta Saudiyya wanda ya tabbatar da halartar ƙasar gaba ɗaya a aikin Hajjin badi.

Farfesa Usman ya bayyana rattaba hannun a matsayin “muhimmin mataki da ke buɗe ƙofa ga tsarin gudanar da Hajj cikin gaskiya, bin doka, da ingantaccen tsari.”

A halin yanzu kuwa, tawagar NAHCON da ke Saudiyya ta kammala duba otal-otal da wuraren girki a Madina domin tabbatar da tsafta, tsaro, da jin daɗin alhazai.

Tawagar ƙarƙashin jagorancin Farfesa Abubakar A. Yagawal, Kwamishinan Sashen Tsare-Tsare, Bincike, Kididdiga, Bayar da Bayanai da Laburare (PRSILS), ta duba otal-otal sama da 20 da kuma wuraren girki 7 a yankin Markaziyya.

Irin wannan aikin na ci gaba a Makka inda Kwamishinoni, Mambobin Hukumar, Wakilan Jihohi da Jami’an Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa ke gudanar da bincike.

A gida kuma, NAHCON na ci gaba da horar da ma’aikatansa ta hanyar gudanar da laccar bayar da horo ta wata-wata inda zaman baya-bayan nan ya mayar da hankali kan “Rawar da National Reception Team ke takawa wajen nasarar aikin Hajji.”

Farfesa Usman ya jaddada cewa waɗannan shiri da sauye-sauye da haɗin gwiwar da ake yi da hukumomin Saudiyya, na nuna cewa Najeriya ta shirya sosai domin gudanar da aikin Hajji 2026 cikin tsari da kwanciyar hankali.

“Jin daɗi, tsaro, da walwalar alhazai na Najeriya sune muhimman abubuwan da muke mayar da hankali,” in ji shi.

Da wannan tallafi daga gwamnati da shirye-shiryen da aka fara tuni, NAHCON na gina sabuwar kafa ta inganci, gaskiya, da tabbatar da walwalar alhazai domin aikin Hajj 2026 mai cike da nasara

Hajj 1026 Kashim Shettima NAHCON Shugaba Tinubu
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Hajjin 2026: Sama da Ma’aikatan Lafiya 700 da Motocin Asibiti 90 Sun Shirya a Madinah

May 2, 2026

Hajjin 2026: Saudiyya Ta Kaddamar da Horaswa Ga Malamai da Jagororin Maniyyata a Madina

May 2, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Hausa

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

By adminMay 4, 20260

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa za ta fara jigilar…

Hajj 2026: Sokoto Hajj Delegation Inspects Hajj Terminal

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Hajj 2026: Sokoto Hajj Delegation Inspects Hajj Terminal

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.