Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    1,357 Pakistani Pilgrims Arrive in Madinah as Hajj 2026 Airlift Commences

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Saudi Arabia Plans Massive Airlift with 12,000+ Flights for Pilgrims

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Health Workers Invited to Join Volunteer Programme

    April 17, 2026

    Saudi Arabia Unveils Major Mina Expansion to Boost Pilgrim Capacity

    April 15, 2026

    Hajj Without Permit Violates Shariah Principles – Sheikh Sudais

    April 15, 2026
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Commences Vaccination of 965 Pilgrims Ahead of 2026 Hajj- By Abdulkadir Aliyu

    April 25, 2026

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024
  • Nahcon

    FG Weighs Policy Options to Cushion Aviation Fuel Costs, Assures Seamless 2026 Hajj Airlift

    April 30, 2026

    Hajj 2026: Inaugural Flight to Takeoff 3rd May – NAHCON

    April 28, 2026

    Kogi Clerics Hail NAHCON Chairman, Seek Sectoral Reforms

    April 26, 2026

    NAHCON Inaugurates Media Team for Hajj 2026, Urges Professionalism and Collaboration

    April 21, 2026

    NAHCON Warns Public Against Fake Hajj Visa Claims, Announces Closure of 2026 Visa Issuance

    April 15, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Gov Ahmad Aliyu and His Transformational Contributions to Hajj Administration in Sokoto

    March 23, 2026

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Hajj Chronicles Ta Fallasa Zargin Makircin Cikin Gida da Ake Yi Don Kawo Matsala Ga Shugabancin NAHCON
Hausa

Hajj Chronicles Ta Fallasa Zargin Makircin Cikin Gida da Ake Yi Don Kawo Matsala Ga Shugabancin NAHCON

adminBy adminDecember 3, 2025No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
1764787661970

Wani bincike na musamman da Jaridar  Hajj Chronicles ta gudanar ya gano abin da ake zargin wani shiri ne na cikin gida da nufin lalata ayyukan Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), bisa ga wasu muhimman takardu da aka fallasa da kuma tattaunawa da wasu manyan jami’an gwamnati da suka san al’amuran da ke faruwa a halin yanzu.

KARANTA LABARI MAKAMANCIN WANNAN : Bincike Ya Nuna Yadda Ake Kirkirar Labaran Karya Don A Bata Sunan Shugaban NAHCON

Wadannan takardu da ake kyautata zaton sun fito ne daga wani rahoton binciken leken asiri na cikin gida sun nuna cewa akwai wata hanyar sadarwa ta wasu mutane a cikin Hukumar da kewaye da ita da ake zargin suna kokarin haifar da rudani a harkokin gudanarwa kafin fara shirin Hajjin 2026.

Takardun na nuni da cewa wannan zargin makircin yana da nufin raunana amincewar jama’a ga shugabancin NAHCON da kuma jefa Fadar Shugaban Kasa cikin mawuyacin hali musamman tsakanin al’ummar Musulmi a Najeriya.

A tsakiyar wannan binciken akwai Shugaban NAHCON, wanda majiyoyi suka bayyana a matsayin mutum mai rikon gaskiya, tsantseni, da shugabanci mai bin umarnin Shugaban Kasa cikin gaskiya da tsari.

A cewar rahoton da aka fallasa, kin amincewarsa da tasirin wasu mutane wajen sarrafa harkokin kudi da tafiyar da hukumar ya haifar da matsin lamba daga wadanda ke neman iko da muhimman bangarorin hukumar.

Wani babban jami’i da ya bukaci a sakaya sunansa saboda tsananin mahimmancin lamarin ya bayyana cewa:

“Kin amincewar Shugaban Hukumar da sabawa ka’idoji ya janyo kokarin kirkirar matsalolin dagula aikinsa.”

Babban abin da rahoton ya bankado shi ne sauyin tsarin da aka yi kwanan nan, inda kulawar NAHCON ta koma daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF) zuwa Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa. Tun bayan wannan sauyi, masu ruwa da tsaki sun ruwaito karuwar karya ka’idojin aiki, ciki har da yadda wasu kananan jami’ai ke wucewa shugaban kai tsaye suna mikawa manyan ofisoshi bayanan sirri ba tare da izini ba.

Masana sun gargadi cewa irin wadannan dabi’u, idan ba a magance su da gaggawa ba, na iya rusa tsarin jagoranci a cikin Hukumar, su takaita yanke shawara, su kuma kawo tsaiko wajen shirin gudanar da Hajjin bana.

Masu fahimtar bayanan leken asiri sun yi gargadin cewa duk wani yunkuri na tayar da hankalin NAHCON zai iya haifar da mummunan tasiri ga kasa baki daya.

Yayin da aikin Hajin 2026 ke dada karatowa, duk wata matsala ko tsaiko a shiri na iya janyo fushin jama’a musamman saboda mahimmancin addini da siyasa da ke tattare da Hajj a Najeriya.

A tarihi, duk wata gazawa a manyan cibiyoyin hidimar jama’a kan janyo wa Shugaban Kasa suka da zargi.

Masana sun yi nuni da cewa matsala a tafiyar da al’amuran Hajj na iya rikidewa zuwa matsalar siyasa da zamantakewa.

Rahoton da aka fallasa ya ba da shawarar a yi nazari cikin gaggawa kan tsarin kulawar NAHCON.

Shawarwarin da aka bayar sun haɗa da mayar da hukumar ƙarƙashin ofishin Sakataren gwamnatin tarayya, ko kuma a mika Hukumar Kiristoci zuwa Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa domin daidaito.

Manyan jami’an da Hajj Chronicles ta tattauna da su sun jaddada cewa gaggawar daukar mataki na da muhimmanci don kaucewa lalata suna, tabarbarewar tsarin aiki, ko tsaikon da zai iya shafar shirin Hajjin shekara mai zuwa.

Hajj Chronicles za ta ci gaba da bibiyar lamarin tare da neman karin bayani daga hukumomin da abin ya shafa.

A lokacin wallafa wannan rahoto, NAHCON, Ofishin Sakataren Gwamnatin tarayya, da Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa ba su amsa bukatar karin bayani ba.

 

Bincike Hajin 2026 Makirci NAHCON
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Hajjin 2026: Sama da Ma’aikatan Lafiya 700 da Motocin Asibiti 90 Sun Shirya a Madinah

May 2, 2026

Hajjin 2026: Saudiyya Ta Kaddamar da Horaswa Ga Malamai da Jagororin Maniyyata a Madina

May 2, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Hausa

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

By adminMay 4, 20260

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa za ta fara jigilar…

Hajj 2026: Sokoto Hajj Delegation Inspects Hajj Terminal

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Hajj 2026: Sokoto Hajj Delegation Inspects Hajj Terminal

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.