Close Menu
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • Hajj News
  • Global
  • Health
  • Nahcon
  • Picture Gallery
  • Opinion
  • Videos
  • HAUSA
Facebook X (Twitter) Instagram
HAJJ CHRONICLES
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram
SUBSCRIBE
  • Home
  • Hajj News

    1,357 Pakistani Pilgrims Arrive in Madinah as Hajj 2026 Airlift Commences

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Saudi Arabia Plans Massive Airlift with 12,000+ Flights for Pilgrims

    April 20, 2026

    Hajj 2026: Health Workers Invited to Join Volunteer Programme

    April 17, 2026

    Saudi Arabia Unveils Major Mina Expansion to Boost Pilgrim Capacity

    April 15, 2026

    Hajj Without Permit Violates Shariah Principles – Sheikh Sudais

    April 15, 2026
  • Global

    Indonesia Plans to Acquire Land for Hajj Village Near Makkah’s Grand Mosque

    July 31, 2025

    Egypt To Halt Land Hajj Trips by 2026 Over Saudi Transport Policy Changes

    July 31, 2025

    UAE Unveils Streamlined Hajj 2026 Accreditation Process to Ensure Transparency and Quality

    July 24, 2025

    flyadeal Aims To Serve 75,000 International Hajj Pilgrims In 2025

    January 23, 2025

    Reflections on the 4th Hajj Conference and Exhibition in Jeddah – By Muhammad Ahmad Musa

    January 21, 2025
  • Health

    Gombe Commences Vaccination of 965 Pilgrims Ahead of 2026 Hajj- By Abdulkadir Aliyu

    April 25, 2026

    Gombe Muslim Pilgrim Board Commences Vaccination for 2025 Hajj Pilgrims – By Abdulqadir Aliyu Shehu

    April 28, 2025

    NAHCON Inaugurates Committee To Review National Medical Team Guidelines for Hajj 2025

    December 19, 2024

    Saudi Health Minister Strengthen Ties With Greece On Health Cooperation During Official Visit

    November 23, 2024

    Umm Al-Qura University volunteers extend help to pilgrims in Mina during Tashreeq

    June 17, 2024
  • Nahcon

    FG Weighs Policy Options to Cushion Aviation Fuel Costs, Assures Seamless 2026 Hajj Airlift

    April 30, 2026

    Hajj 2026: Inaugural Flight to Takeoff 3rd May – NAHCON

    April 28, 2026

    Kogi Clerics Hail NAHCON Chairman, Seek Sectoral Reforms

    April 26, 2026

    NAHCON Inaugurates Media Team for Hajj 2026, Urges Professionalism and Collaboration

    April 21, 2026

    NAHCON Warns Public Against Fake Hajj Visa Claims, Announces Closure of 2026 Visa Issuance

    April 15, 2026
  • Picture Gallery
  • Opinion

    Gov Ahmad Aliyu and His Transformational Contributions to Hajj Administration in Sokoto

    March 23, 2026

    Nigeria Hajj Industry: Back To Square One – By Abubakar Jidda Usman

    February 11, 2026

    NAHCON Reconciliation Viewed as Positive Step for Hajj Administration – By Muhammad Sulaiman Gama

    February 2, 2026

    NAHCON Board’s Vote of No Confidence: A Mask for Self-Interest.

    February 1, 2026

    Nigeria Hajj Industry: When Would Pilgrims’ Interest Supercede Personal Interest of Handlers and Stakeholders

    January 31, 2026
  • Videos
  • HAUSA
HAJJ CHRONICLES
Home » Rikicin Jigilar Alhazan 2026: Zargin Makircin Cikin Gida A NAHCON Na Barazana Ga Yarjejeniyar Sufurin Jirage Tsakanin Najeriya Da Saudia
Hausa

Rikicin Jigilar Alhazan 2026: Zargin Makircin Cikin Gida A NAHCON Na Barazana Ga Yarjejeniyar Sufurin Jirage Tsakanin Najeriya Da Saudia

adminBy adminJanuary 12, 2026Updated:January 12, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter LinkedIn WhatsApp Email Telegram
FB IMG 1766066402041

Daga Abubakar Idi Maru, Abuja Shirye-shiryen aikin Hajjin 2026 na Nijeriya na fuskantar babbar barazana, sakamakon ƙara taɓarɓarewar dangantaka tsakanin Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) da Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Masarautar Saudiyya (GACA).

Rahotanni na nuni da cewa hukumomin sufurin jiragen saman Saudiyya na tunanin ɗaukar matakan hukunci, ciki har da yiwuwar hana jiragen Nijeriya samun izinin sauka, bisa zargin cewa Nijeriya ta kasa bin ka’idojin Yarjejeniyar Sufurin Jiragen Sama ta Ƙasashe Biyu (BASA) da aka cimma a 2015.

A cikin rikicin akwai gazawar NAHCON wajen tura cikakken jadawalin tashin jiragen Hajji ga GACA, wanda yake zama wajibi kafin a ba da izinin sauka da wucewa ta sararin samaniya a lokacin aikin Hajji.

Masana harkar jiragen sama na gargaɗin cewa ci gaba da jinkirta aika wannan jadawali na iya jefa Nijeriya cikin matakin hukunci daga Saudiyya, tare da haifar da babbar matsala ga dukkan tsarin jigilar alhazai.

Bincike ya nuna cewa rabon jihohi da jiragen sama da NAHCON ta fitar a watan Disambar 2025 bai yi la’akari da ragin yawan alhazai daga jihohin da aka bai wa kamfanin jirgin Saudiyya Flynas ba, yayin da aka ƙara wa jiragen Nijeriya kaso mai yawa. Maimakon a daidaita adadin domin cika sharadin rabon kashi 50–50 na BASA tare da fitar da jadawalin jirage mai inganci, ana zargin Hukumar ta bar wannan rashin daidaito ya ci gaba, lamarin da ya ƙara rikitar da tsarin shirye-shiryen GACA.

Wasu manyan majiyoyi a cikin NAHCON na zargin cewa lamarin ya wuce sakaci ko rashin ƙwarewa, suna danganta shi da ganganci da mugun nufi daga Kwamishinan Ayyuka na Hukumar, Prince Anofiu Elegushi. A cewar waɗannan majiyoyi, an yi watsi da matakan gyara da gangan duk da sanin cewa rashin amincewar jadawalin jirage na iya bai wa hukumomin Saudiyya damar takaita ko ma dakatar da jigilar alhazan Nijeriya, abin da zai cutar da walwalar alhazai da martabar Gwamnatin Tarayya a idon duniya.

Rikicin ya ƙara tsananta ne da ikirarin cewa wani tsohon mataimaki mai ritaya na ci gaba da tsoma baki a harkokin jiragen sama ba tare da wata doka ko izini ba.

Masana harkar sufurin jiragen sama na gargaɗin cewa wannan haɗakar tsoma bakin ciki, tangardar tsarin gudanarwa da rashin bin ƙa’idoji na iya sake tayar da rikicin da aka warware tun 2015, inda suka tunatar da cewa Nijeriya na cikin ƙasashe kaɗan da Saudiyya ta bai wa sassauci wajen aiwatar da BASA a hankali wata dama da ba a bai wa ƙasashe da dama masu aikin Hajji ba.

Da yake rahotanni ke nuna cewa hukumomin Saudiyya sun fara gajiya, masu ruwa da tsaki na jaddada cewa duk wani matakin hukunci da za a ɗauka zai fi shafar alhazan Nijeriya ta fuskar jinkirin jirage, rage kujeru ko ma hana shiga filayen jiragen saman Saudiyya a lokacin kololuwar aikin Hajji.

A sakamakon haka, ana kira da a gaggauta sa bakin Gwamnatin Tarayya, a hanzarta tura jadawalin jiragen Hajji da ya dace da BASA zuwa GACA, tare da gudanar da bincike a bayyane kan zargin ganganci na ciki, domin kauce wa rikicin da ka iya zama babbar matsala ta ƙasa, ta diflomasiyya da ta jinƙai.

Abubakar Idi Maru,
Ɗan jarida mai bincike,
Abuja.

GACA Hajj 2026 Makircin Cikin Gida Najeriya Saudi
Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp

Related Posts

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

Don't Miss
Hausa

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

By adminMay 4, 20260

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa za ta fara jigilar…

Hajj 2026: Sokoto Hajj Delegation Inspects Hajj Terminal

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Stay In Touch
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • WhatsApp
Our Picks

An Kammala Bitar Alhazai a Kano, Jigilar Maniyyata za ta Fara 14 ga Mayu

May 4, 2026

Hajj 2026: Sokoto Hajj Delegation Inspects Hajj Terminal

May 4, 2026

Gombe Intensifies Preparations for 2026 Hajj as Stakeholders Chart Path for Seamless Operations

May 2, 2026

Niger Pilgrims Board Holds Pre-Haj Workshop for 2026 Hajj

May 2, 2026
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Home
  • About Us
  • Privacy Policy
  • Contact Us
© 2026HAJJ CHRONILES

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.